1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hong Kong: Illolin rikici kan tattalin arziki

Usman Shehu Usman RGB
August 21, 2019

Chaina na fargaba rikicin yankin Hong Kong ka iya shafar tattalin arzikinta yayin da masu zanga-zangar Hong Kong ke cewa kasar na kara karfi wajen juya al-amuran tafiyar da gwamnati.

https://p.dw.com/p/3OH3S
Hongkong Protestkundgebung vor dem Chater Garden
Hoto: picture-alliance/AP Photo/K. Cheung

Duk da wannan fafutukar da masu zanga-zangar na yankin Hong Kong ke yi don tilasta ma Chaina fita daga dukkan lamuran kasar, akasarin 'yan kasar ta Chaina ba su ma san me ke faruwa a yankin ba. Sai dai masana sun yi hasashe kan tasirin da rikicin zai iya yi ga sha'anin kasuwanci musanman a babban birnin kasar ta Shanghai.


Yanzu haka dai hukumomin kasar Chaina sun kwan da cewar rikicin da ke faruwa a Hong-Kong kan iya yin tasiri a birnin kasuwanci kamar Shanghai, suma mazauna birnin suna tsoron abin da ka iya faruwa a birninsu, in aka ci gaba da yi wa gwamnati tawaye a Hong-Kong. A yanzu dai gwamnatin Beijing na daukar duk matakai da suka dace na kawo karshen rikicin Hong-Kong da kuma hana shi bazuwa cikin kasarta.