1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yunkurin dara Ghana gida biyu ya sa kotu ta daure 'yan aware

Mouhamadou Awal Balarabe
March 7, 2024

Kotu ta samu kungiyar aware ta WTRF da laifin kai hari kan ofisoshin 'yan sanda tare da toshe hanyoyin da ke kusa da kan iyaka da Togo a 2020, a wani mataki na neman 'yancin kai na wani yanki mai suna Western Togoland.

https://p.dw.com/p/4dHZM
Kotun kolin kasar Ghana na taka rawa wajen daidaita shari'o'i
Kotun kolin kasar Ghana na taka rawa wajen daidaita shari'o'iHoto: cc-by/aripeskoe2

Wata kotu a Ghana ta yanke wa wasu mutane hudu da suka hada da dan sanda da soja hukuncin daurin shekaru biyar a gidan yari, saboda samun su da laifin jagorantar kungiyar 'yan aware ba bisa ka'ida ba.  A yayin yanke hukunci a Accra, mai shari'a Mary Maame Ekueh Yanzuh ta ce  "Wannan hukuncin ya zama gargadi mai karfi game da duk wani yunkuri na yin barazana ga zaman lafiyar kasar Ghana."

Karin bayani: Martani kan dokar hana auren jinsi a Ghana

Shi wanda ya kafa kungiyar Michael Koku Kwabla ya sha daurin shekaru biyar a wakafi da tarar dalar Amurka 940 (kusan Euro 860), yayin da sauran mambobin kungiyar Nene Kwaku da Emmanuel Afedo da Abednego Mawena aka yanke musu hukuncin daurin shekaru hudu a gidan yari kowannen su. tun a shekarar  2017 ne aka kama shugabannin 'yan aware a yankin kogin Volta da ya kunshi kabilu da yawa, saboda  haka ne suke so su mayar da yankin ya zama kasa mai cin gashin kanta.