Yaya Toure ya sake zama gwarzo a Afirka
January 9, 2015Talla
An gabatar da shahararren dan wasan kwalon kafan nan na kasar Ivory Coast Yaya Toure a matsayin gwarzon dan wasan Afrika na wannan shekara.
Ya ce "a gaskiya, ba wai a harkar wasan kwallon kafa kawai ba, na sha fatan cinma nasara a abubuwa da dama. Sai dai a fannin wasa wannan ba abu ne mai sauki ba, musamman ma yanzu da muke da kwararrun matasa da suka shiga wannan harkar, kuma suna taka rawa mai kyau".
Tuni dai kungiyar kwallon kafa da ya ke wa wasa ta Manchesta city ta aike masa da sakon taya murna, tare da nuna alfahari da shi. Masu horar da 'yan wasa na Afrika da direktocin harkokin wasanni ne dai, suke zartar da wanda ya cancanci wannan lambar yabo na gwarzon kwallon kafar Afrika.