1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gwamnati da Abzinawa a Mali sun tsagaita wuta.

Lateefa Mustapha Ja'afarJune 5, 2015

Gwamnatin kasar Mali da 'yan tawayen Abzinawan kasar sun sanya hannu kan wata yarjejeniya da ta amince da tsagaita a tsakaninsu.

https://p.dw.com/p/1FcTp
'Yan twayen Abzinawa na Mali da ke rikici da gwamnati
'Yan twayen Abzinawa na Mali da ke rikici da gwamnatiHoto: picture-alliance/AP Photo//Rebecca Blackwell

Hakan dai ya bada karfin gwiwa wajen cimma yarjejeniyar sulhu da Majalisar Dinkin Duniya ta jima ta na kokarin ganin an cimma a tsakaninsu domin kawo karshen yakin da suka kwashe tsahon shekaru suna fafatawa da juna a arewacin kasar. Babban jakadan Majalisar Dinkin Duniya a Malin Mongi Hamdi ne ya sanar da hakan inda ya ce daya daga cikin matakan yarjejeniyar ya bukaci da a tsagaita wuta a garin Menaka da ke arewaci da kuma janyewar mayakan sa kai da ke goyon bayan gwamnatin ta Mali a yankin, inda ya ce za a maye gurbinsu da dakarun Majalisar Dinkin Duniya zuwa wani lokaci. Su dai 'yan tawayen Malin na fafutukar samar da 'yancin kan yankin Abzinawa ne wanda suka yiwa lakabi da Azawad.