'Yan ta'adda sun kashe sojoji a Mali
March 17, 2019Talla
Wasu 'yan bindiga da ake zargin 'yan ta'adda ne sun kashe sojoji takwas a wani hari kan sansanin sojoji da ke tsakiyar kasar Mali. Sai dai akwai fargabar adadin mutuwar ya karu. Rundunar sojin kasar Mali ta ce sojojin sun fafata da 'yan ta'addan da suka kaddamar da harin.
Kasar Mali ta fuskanci hare-hare akalla 237 a shekarar 2018 duk da cewa akwai rundunar kiyaye zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya a Mali da sojojin Faransa hada da rundunar sojojin hadin gwiwa na kasashen yankin Sahel.