1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan gudun hijira a Muzambik na bukatar agaji

July 6, 2021

Hukumar abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci makudan kudade da suka kai dalar Amirka miliyan 121 domin tallafa wa al'ummar da hare-haren yan bindiga ya daidata a lardin Cabo Delgado da ke arewacin Muzambik.

https://p.dw.com/p/3w7c3
Hungersnot in Madagaskar
Hoto: Welternährungsprogramm WFP/dpa/picture alliance

Sama da mutun 730,000 ne ke cikin hatsarin afkawa cikin matsanancin karacin cimaka a yankin, ma damar ba a kai masu daukin gaggawa ba, ta bakin daraktan hukumar abinci na majalisar David Beasley bayan wata ziyarar gani da ido da ya kai a yankin.

Yankin na Cabo Delgado mai arzikin iskar gas ya kasance cikin rikici tun a shekara ta 2017 lokacin da masu ikirarin jihadi suka fara kai hare-haren ta'adanci da suka hallaka al'umma da dama wasu kuma suka tsallake matsugunnansu.