'Yan fashin ruwan teku sun kai hari ga wani jirgin ruwa a Najeriya
December 24, 2012Talla
Hukumar kula da zirga-zirgan jiragen ruwa ta ƙasa da ƙasa ta bayana cewar wasu 'yan bindiga da ba a san ko su wane ba,sun kaiwa wani jirgin ruwa mai sufirin man fetur hari a kudancin Najeriya,inda kai tsaye suka yi awon gaba da wasu turawa guda huɗu da ke cikinsa. Ko da yake rahotani daga kamfanin dillancin labaran Faransa da ya ruwaito wannan labarin,ya ce duk da harin da aka kai masa,jirgin ruwan ya samu nasarar kaiwa wata mashigar ruwa inda ya samu tsira. Tuni dai masu nazarin al'amura ke nuna fargaban ganin kudancin Najeriyar ya kasance wani sabon filin daga ruwan teku,ƙasasr da ke yawan fuskantar wannan matsalar.
Mawallafi: Issoufou Mamane
Edita: Yahouza Sadissou Madobi