'Yan bindiga sun kashe sojiji 16 a kasar Mali
October 1, 2019Talla
Maharan sun isa cikin unguwar da barikin hadayar sojan G5 Sahel da manya-manyan bindigogi a cewar wani kwamandan Sojin kasar Nijar Oumarou Namatou Gazama inda ya dora alhakin harin a kan wata kungiya mai suna Ansarul Islam.
Wani mutum da ke yankin wanda ya nemi a sakaya sunansa ya tabatar da ganin gawawakin sojoji goma sha biyu akwance a kasa.
Wannan harin da aka kai a barikin sojin ya yi sanadiyar bacewar manyan bindigogi da ma wasu kayaykin yaki mallakar sojojin a cewar mai magana da yawun gwamnatin kasar ta Mali Yaya Sangare.