Yaƙi ya sake ɓarkewa a Jamhuriyar Demokraɗiyyar Kwango
November 18, 2012A cikin wata sanarwa da wakilan kwamitin sulhun na Majalisar Ɗinkin Duniya suka baiyana,a wani taron gauggawa da suka kira sun buƙaci ƙungiyar ta 'yan tawayen M23 da ta daina kai hare haren.
Yan tawayen waɗanda suka yi dura mikiya a ƙauyen Kikumba, sun yi nasara ƙwace shi daga hannu sojojin gwamnatin;duk Kuwa da irin martanin da suka riƙa mayar wa da jiragen sama na yaƙi masu saukar ungulu.Duban jama'a na ta yin ƙaura daga garin domin kwararawa zuwa wasu ƙayuka na kusa saboda fargaban da suke da shi na ƙara dagulewar al'ammura
Tun da farko dai hukumar Majalisar Ɗinkin Duniya ta Monusco da ke gudanar da aikin tabbatar da tsaro a yanki ta yi shelar wani hali na kasance wa cikin shirin ko ta kan kwana a yanki.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Usman Shehu Usman