1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

WHO na rigakafin polio a kasashen Afirka

March 24, 2017

Hukumar Lafiya ta Duniya zata yi wa miliyoyin yaran Afirka allurar rigakafin cutar shan Inna bayan da mutane uku suka kamu da cutar da Polio a tarayyar Najeriya a shekarar da ta gabata.

https://p.dw.com/p/2ZvST
Nigeria Polio-Impfung
Hoto: Global Polio Eradication Initiative

Kasashe 13 na Afirka na shirin gudanar da allurar rigakfin cutar shan Inna ko Polio na bai daya a ranar Asabar, bayan da aka tabbatar da cewar mutane uku sun kamu da ita a shekarar da ta gabata a arewacin tarayyar Najeriya. Cikin wata sanarwa da ta fitar Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce za a yi wa yara miliyan 116 rigakafin shan Inna a kasashen da dama ciki har da Jamhuriyar Nijar da Kamaru da Chadi da Jamhuriyar Benin.

WHO ta nunar da cewar mutane hudu ne suka kamu da cutar Polio a cikin wannan shekara ta 2017, biyu a Afghanistan, biyu kuma a Pakistan. Sai dai kuma ta ce zata rubanya rigakafi a kasashen Afirka saboda kaurin suna da nahiyar ta yi a fannin yawan wadanda suka kamu da Polio.

Tarayyar Najeriya ta taba kasancewa a sahun gaba na kasashen da aka fi fama da Polio a duniya. Sai dai WHO ta cireta daga wannan rukuni tun a shekara ta 2015 bayan da ta dauki matakan da suka dace.