1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Wasu matan da aka sace a Borno sun tsere

July 7, 2014

Rahotanni daga jihar Borno dake Arewa maso gabashin tarayyar Najeriya na nuni da cewa 63 daga cikin matan da aka sace a watan da ya gabata sun tsere.

https://p.dw.com/p/1CWlf
Nigeria Protest Boko Haram Entführung
Hoto: picture-alliance/AP Photo

Daya daga cikin 'yan kato da gora da ke taimakawa wajen yakar 'yan Boko Haram a jihar ta Borno Abbas Gava ya bayyana cewa wani abokin aikinsa ya shaida masa cewa 63 daga cikin matan sun koma gida tun ranar Jumma'ar da ta gabata. Gava ya shaida wa manema labarai cewa matan sun samu nasarar tserewa ne a yayin da masu tsaronsu suka fita kai farmakin da suka saba.

Shi ma wani babban jami'in tsaro a jihar ta Borno da ya bukaci a boye sunansa ya tabbatar da nasarar tserewa gida da matan suka samu. Ko da a ranar Jumma'ar da ta gabata ma dai sai da aka yi musayar wuta tsakanin 'yan ta'addan da jami'an tsaro a garin Damboa na jihar ta Borno inda rahotanni ke cewa akalla sama da 'yan ta'addan 50 ne suka sheka barzahu yayin wannan fafatawar.

Mawallafiya: Lateefa Mustapha Ja'afar
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe