1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan sandan Afirka ta Kudu sun wargaza zanga-zanga

Binta Aliyu Zurmi SB
February 13, 2022

'Yan sanda sun yi amfani da harsashen roba a kan masu boren kin jinin baki a Afirka ta Kudu.

https://p.dw.com/p/46xWw
Südafrika Proteste gegen Arbeitsmigranten
Hoto: Guillem Sartorio/AFP

'Yan sandan kwantar da tarzoma a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu sun yi amfani da harsashen roba wajen tarwatsa masu zanga-zangar kin jinin ayyukan da baki ke yi a kasar.

Daruruwan mutanene suka fito zanga-zangar ta yau, sai dai jami'an tsaro sun yi nasarar tarwatsasu, yayin da suka tunkari wasu shagunan baki a birnin na Johannesburg.

Kasar ta Afirka ta Kudu da ke zama kasa mafi ci-gaban masana'antu a nahiyar Afirka tana samun mutane daga kasashe a nahiyar da ke zuwa domin neman aiki, sai dai suna cin karo da kalubalen tsana da tsangwama gami da kin jinin baki.