1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Maduro zai rufe iyakarsa da sauran kasashe

Abdul-raheem Hassan
February 21, 2019

Gwamnatin Shugaba Nikolas Maduro ta ce matakin rufe iyakokin Venezuela da kasashen Kwalambiya da Brazil zai hana kasashen waje shigo da kayan agaji zuwa cikin kasar.

https://p.dw.com/p/3Dopj
Nicolas Maduro
Hoto: picture-alliance/dpa/Z. Campos

Matakin gwamnatin na Venezuela na zuwa ne a dai dai lokacin da madugun adawar kasar da ke ikirarin shugabanci Juan Guido ya je kan iyakar kasar da Kwalambiya tare da wasu lauyoyi 80 domin duba yiwuwar shigo da kayan agaji da kasar Amirka ta aiko.

Jagoran adawa Guido tare da kasashen da ke mara masa baya na zargin Shugaba Maduro da jefa al'ummar kasar cikin yunwa da talauci sakamakon matsin tattalin arziki da kasar ke ciki.

Sai dai Shugaba Maduro da ke samun goyon bayan kasashen Rasha da China, ya zargi Amirka da neman yi wa gwamnatinsa zagon kasa tare da yi wa dimukuradiyya karan tsaye.