1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Turai za ta tura dakarunta Bangui

January 20, 2014

Turai ta ce ta yanke shawarar tura dakarunta Jamhuriyar Afirka ta Tsakiyar ne domin taimakawa wajen inganta ayyukan jinƙai

https://p.dw.com/p/1Atma
Zentral Afrikanische Republik UN Truppen nach Bangui
Hoto: ISSOUF SANOGO/AFP/Getty Images

A yayin da Majalisar dokokin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ke ƙoƙarin zaɓen sabon shugaban ƙasa,

Ministocin kula da harkokin wajen Turai sun yanke shawarar tura dakarun Nahiyar zuwa ƙasar domin marawa dakarun Faransan dake wanzar da zaman lafiya a yankin.

Faransa wadda ta tura dakaru dubu ɗaya da ɗari shidda a watan da ya gabata na neman tallafi, kuma ministocin na ƙasashe 28 dake nahiyar sun ce ana buƙatar aƙalla dakaru 400 zuwa 600

Bisa bayyanan kamfanin dillancin Associated Press, Jami'an diplomasiyyan Turai suna buƙatan tura dakarun ne domin su mayar da hankali kan Bangui, da filin jirgin saman ƙasar, kana kuma su gudanar da sauran ayyukan jinƙan da ake buƙata a tsukin watanni shidda.

Mawallafiya: Pinaɗo Abdu Waba
Edita: Saleh Umar Saleh