1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tsadar rayuwa a Tuniyasa

Zainab Mohammed Abubakar
May 2, 2019

Ma'aikatan kamfanonin man petur a Tunisiya sun fara yajin aikin kwanaki uku, don neman karin albashi, yajin aikin da ya haifar da karancin mai a dukkan gidajen man fetur da ke fadin wannan kasa

https://p.dw.com/p/3Hp8Z
Tunesien Landesweiter Streik
Hoto: Reuters/Z. Souissi

 

Gwamnatin Tunis din dai na cigaba da fuskantar tirjiya daga bangaren al'umma da ke neman karin albashi, biyo bayan tsadar rayuwa da faduwar darajar kudin kasar, daura da matsin lamba na masu bayar da bashi na kasa da kasa, kan bukatar aiwatar da mataki na tsuke bakin aljihu.

A jiya Laraba ne dai, hukumomin kasar suka sanar da karin mafi kankantan albashin ma'aikatan masana'antu da gonaki, da ma masu karbar pansho da wajen kashi 6.5, wanda ke da nufin sassauta wahalar rayuwa.

Sai dai yajin aikin da ma'aikatan man fetur din suka kaddamar na bukatar karin a kalla dalar Amurka 100 a wata, shi ne na baya bayannan da ke haifar da tsaiko a harkokin ilimi da kiwon lafiya da ma bangaren sufuri.