1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin siyasa a Tunisiya

Zulaiha Abubakar
August 24, 2019

Mahukuntan kasar Tunisiya sun kame  Nabil Karoui  dan takarar shugabancin kasar bayan tuhumarsa da rashin biyan kudaden haraji da kuma musayar kudi ba bisa ka'aida ba.

https://p.dw.com/p/3OPgC
Tunesien Tunis | Medienmogul Nabil Karoui
Hoto: Getty Images/AFP/Hasna

Nabil Karoui mai shekaru 56 a duniya ya yi fice wajen sukar lamirin gwamnatin kasar ta wani gidan talabijin mai zaman kansa mallakinsa, tun bayan rasuwar shugaban kasar Beji Caid Essebsi a watan da ya gabata. A ranar juma'ar da ta gabata ne hukumar kula da sadarwa ta kasar da hadin gwiwar hukumar zabe a Tunisiyan suka dakatar da wasu manyan kafafen yada labarai daga aiki wadanda suka hadar da gidan talabijin na Nessma mallakar Karoui da ke zaman dan takarar shugabancin kasar .

An dai jiyo Karoui na bayyana tuhumar da ake masa da yarfe don a rage masa farin jini da karbuwa tsakanin al'ummar kasar. A ranar 15 ga watan Satumba mai kamawa za a gudanar da zaben shugaban kasa a Tunusiyan, bayan rasuwar tsohon shugaban kasar marigayi Beji Caid Essebsi wanda ya yi nasarar zama shugaban kasar na farko a tafarkin Dimukuradiyya.