Kwango: An sarki fursunonin siyasa
March 14, 2019Talla
Daga cikin wadanda aka sako har' da wasu fitatun 'yan siyasa wadanda suka yi adawa da tsofuwar gwamnatin Joseph Kabila. Wadanda suka hada da Franck Diongo, da Diomi Ndongala da kuma Firmin Yangambi. Tun farko kafin zaben da aka yi a kasar a cikin watan Disambar shekara bara Tshisekedi ya sha alwashin cewar zai saki dukkanin fursunonin siyasar idan har shi ya ci zaben.