1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Tattalin arziki

Koma baya a tattalin arzikin Afirka ta Kudu

Suleiman Babayo
September 4, 2018

Tattalin arzikin Afirka ta Kudu ya samu koma baya lamarin da ke zama nakasu ga Shugaba Cyril Ramaphosa wanda zai fuskanci zabe a shekara mai zuwa ta 2019.

https://p.dw.com/p/34IVl
Südafrika Atomkraftwerk Koeberg nahe Kapstadt
Hoto: picture-alliance/dpa/EPA/N. Bothma

Kasar Afirka ta Kudu ta shiga cikin matsalar koma bayan tattalin arziki da kashi 0.7 cikin 100 kamar yadda alkalun da hukumomin suka fitar suka nuna abin da ke zama nakasu ga Shugaba Cyril Ramaphosa wanda ya dauki madafun iko kasar a watan Febrairun da ya gabata.

Wannan shi ne karo na biyu a zubi hudu na shekara da tattalin arzikin kasra ta Afirka ta Kudu ke samun koma-baya, lamarin da yake da danganta da farin da aka samu a Yammacin Cape da kuma ambaliyar ruwa da ta lalata amfanin gona a gundumar Mpumalanga.

A shekara mai zuwa ta 2019 Shugaba Cyril Ramaphosa na kasra ta Afirka ta Kudu zai fuskanci zabe cikin matsalolin neman masu zuba jari da rashin ayyuka da suka yi wa matasan kasar katutu.