1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tasirin Olusegun Obasanjo a jam'iyar PDP

Usman ShehuApril 4, 2012

'Yan Najeriya sun fara maida martani bisa murabus ɗin da Cif Olusegun Obasanjo ya yi daga muƙamin shugaban amintattun PDP.

https://p.dw.com/p/14Xj3
Re-elected President Olusegun Obasanjo smiles as he leaves a ceremony where he was presented with a certificate of return by the Independent National Electoral Commission at the INEC headquarters in the Nigerian capital Abuja Wednesday, April 23, 2003. (AP Photo/Ben Curtis)
Hoto: AP

A Najeriya murabus ɗin da shugaban kwamitin amintatu na jamiyyar PDP Cif Olusegun Obasanjo ya yi bisa kan wannan mukami bayan daɗewar da aka yi ana ja in ja da ma nuna bugƙatar hakan ya sanya tambayar tasirin da sauakar tasa za ta yi ga jamiyyar da ma dimukurɗiyyar Najeriyar.

To fararre dai kararre ne in ji Hausawa domin kuwa bayan daɗewar da aka yi ana zura ido, kiraye-kiraye da ma amfani da harka da irin ta siyasa tsohon shugaban Najeriyan da ke zama jigo a jamiyyar ta PDP da ke mulkin Najeriyar tun daga 1999 ya yi murabus daga mukaminsa na shugaban kwamitin amintatu na jamiyyar ta PDP.

Britain's Queen Elizabeth II watches as Nigeria's President, Olusegun Obasanjo, holds up a white cloth as a symbol of peace at the opening session of the Commonwealth Summit in Abuja, Nigeria, Friday Dec. 5, 2003. (AP Photo/Saurabh Das, POOL)
Hoto: AP

Tasirin Obasanjo a PDP

Sanin irin tasirin da wannan kwamiti ke da shi a fanin juya akalar inda jamiyyar ta dosa da ma maƙalewar da Cif Obasanjon ya yi a kan wannan muƙami da bisa al'ada ya kamata da daɗewa ya sauka daga kansa ya sanya tambayar tasirin da wannan ka iya yi ga jamiyyar musamman batun dimokɗiyya ta cikin gida ta jamiyyar da yadda mulkin dimukurɗiyyar ke tafiya a Najeriyar. Malam Bukhari Muhammad darakta ne a cibiyar nazarin dimukurɗiyya da ci gaban ƙasa da ke Abuja. Wanda tabbas saukar Obasanjo a muƙamin shugaban amintattu na jam'iyar PDP yana da tasiri.

Rawar da Obasanjo ya taka a PDP

Bisa la'akari da irin rawar da tsohon shugaban Najeriyar Cif Obasanjo ya taka wajen samuwar gwamnatin Najeriya a karkashin shugaba Goodluck Jonathan da ma yadda yake kai ƙwauro yana kai mari a ƙoƙarin jamiyyar na sake kame jihohin kudu maso yammacin Najeriya da jamiyyar adawa ta ACN ta yi masu cin kaca a zaben da aka yi a bara, ya sanya tambayar ko dai Cif Obasanion ya fara rasa tasirinsa ne a jamiyyar ta PDP ya sanya shi ɗaukar wannan mataki, abinda Malam Bashir Baba da ke sharhi a kan al'ammuran Najeriya ya bayyana da cewa akwai alama.

President Goodluck Jonathan speaks during the ruling party primary in Abuja, Nigeria, Thursday, Jan. 13, 2011. Delegates of Nigeria's ruling party began voting Thursday night to pick its presidential candidate, choosing between honoring a power-sharing agreement by selecting a Muslim or endorsing the oil-rich nation's current Christian leader. (AP Photo/Sunday Alamba)
Hoto: AP

A yayinda za'a ci gaba da sa ido ga irin salon mulkin da sabon shugaban jamiyyar PDP Alhaji Bamanaga Tukur zai yi a jamiyyar ta PDP da ke zama mai tsole idanu ga yadda siyasa ke tafiya a Najeriya, abu muhimmi shine jiran ganin ko Cif Obasanjo ya ja gefe ne ko kuwa akasin hakan ne zai faru.

Mawallafi: Uwais Abubakar Idris
Edita: Usman Shehu Usman