1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron koli ya duba matsayin Turai kan 'yan gudun hijira

October 25, 2013

Ƙasashen Turai sun buƙaci da a inganta tsaro kan iyakokinsu domin kariya da kuma tsare lafiyar 'yan gudun hijira sai dai ba su ɗauki mataki kan yadda za a shawo kan matsalar ba

https://p.dw.com/p/1A6PH
ARCHIV - Ein Boot mit Flüchtlingin, aufgenommen am 26.03.2011 in Lampedusa. Wenn es um illegale Flüchtlinge geht, liegen die EU-Staaten seit Jahren im Clinch. Der Ansturm von Flüchtlingen aus Nordafrika in Richtung Italien stellt das vielgerühmte Europa ohne Grenzen auf eine harte Probe. Foto: EPA/VENEZIA FILIPPO dpa (zu dpa 0911 vom 25.04.2011) +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: picture-alliance/dpa

A kowace rana, ƙananan jiragen ruwa ɗauke da 'yan gudun hijira ke shiga ƙasar Italiya, kuma wannan ta zama masu babbar matsala. A dalilin haka ne mahukuntan Italiya suka yanke shawarar cewa wajibi ne ƙasashen Turai baki ɗaya su raba alhakin ɗaukan 'yan gudun hijiran, sai dai duk da haka, banda batun tsaron iyakokin ƙasashen Turai da tabbatar lafiyar 'yan gudun hijiran, yawancin wakilan ƙasashen da suka kasance a taron ƙolin Ƙungiyar Tarayyar Turai na wannan karon ba su bada wata gudunmawa wajen shawo kan wannan matsala ba.

Daga cikin waɗanda suka halarci taron ƙolin na Ƙungiyar Tarayyar Turan da ya gudana a birnin Brussels yau har da magajin garin Lampedusa na ƙasar Italiya Guisi Nicolini, wadda ta zo ta gabatar da ƙorafinta ga shugabanin gwamnatocin nahiyar, domin samun goyon bayansu.

Tanadin dokokin Turai kan karɓar baƙi

Gwamnatin Italiya na ganin nauyin ya yi mata yawa na kula da 'yan gudun hijiran da ke shiga ƙasar a kowace rana ta Allah, kuma a ganinta kamata yayi suma sauran ƙasashen su raba wannan nauyi. Firaministan Italiya Enrico Letta wanda ya tabbatar wannan batu ya kasance kan gaba a taron ya ce suna buƙatar mataki mai ƙwari

Los Cristianos, SPAIN: Italian boat "San Giorgio" is seen at the port of Los Cristianos in the Spanish Canary Island of Tenerife 18 August 2006. The boat was operating for the FRONTEX European Union external border agency, a plan for helping Spain against the massive entrance of illegal immigrants. The Frontex operation involve two patrol boats, from Italy and Portugal, operating off Mauritania and Cape Verde, along with two surveillance planes provided by Finland and Italy, joined by Spanish patrol boats and helicopters already operating in the area. The Canaries, between 100 and 400 kilometres (60 and 250 miles) from the African coast, became the preferred route for clandestine migrants after security was heightened in Spanish enclaves in north Africa. AFP PHOTO / Desiree Martin (Photo credit should read DESIREE MARTIN/AFP/Getty Images)
Jirgin ruwan masu tsaron kan iyaka na FrontexHoto: Desiree Martin/AFP/Getty Images

"A gani na, tilas ne mu ɗauki mataki na bai ɗaya a matsayinmu na Turai, kuma daga abin da na gani yau, a ra'ayi na matakin da aka ɗauka mai ma'ana ne, yanzu mun san cewa Ƙungiyar Tarayyar Turai ta ɗauki wannan batu da mahimmanci, kuma a gani na matakin da aka dauka na da mahimmanci"

Sai dai bisa tanadin dokokin Turai, duk wani ɗan gudun hijira, zai iya samun takardar izinin zama ko kuma mafaka ne a ƙasar Turan da ya fara taka ƙafa, saboda haka, duk ɗan gudun hijirar da ya shiga Turai ta Italiya misali, sai kuma daga nan ya tafi Jamus, jami'an kan iyakar Jamus zasu iya tasa ƙeyarsa zuwa Italiya tunda nan ya fara sanya ƙafa, amma a waje guda kuma, shugabanin na ganin cewa ko da shi ke matsala ce da ta shafi nahiyar baki ɗaya, ƙasashensu ba su da ƙarfin karɓar yawan mutanen da ke shigowa nahiyar.

President of the French far-right Front National (FN) party Marine Le Pen acknowledges the crowd after a meeting during a visit in the French northeastern village of Brachay on October 6, 2013. AFP PHOTO / FRANCOIS NASCIMBENI (Photo credit should read FRANCOIS NASCIMBENI/AFP/Getty Images)
Shugabar jami'yyar masu ra'ayin mazan jiya a FaransaHoto: AFP/Getty Images

Hana gudun hijirar tun farko

Yawancinsu, a ɓoye ma suna farin cikin kasancewar irin wannan doka, domin 'yan gudun hijira ƙalilan kaɗai suke so su ɗauka, hasali ma gara musu idan ma tun farko basu baro ƙasashensu na ainihi ba. Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta nunar da cewa ya kamata a tabbatar da tsaro kan iyakokin dan kare hatsari daga afkuwa

" Akwai mahimmancin gaske a ce an sami haɗin kai wajen tabbatar da tsaron 'yan gudun hijirar daga ƙasar da suke fitowa, zuwa ƙasar da suke shiga. Batun ƙarfafa hukumar tsaron iyakoki na Frontex ya taka muhimmiyar rawa wajen tattaunawar da aka yi domin babu shakka suna ƙoƙarin yaƙi da miyagun ayyuka amma kuma mun san cewa wannan aikin yana tattare da sarƙaƙiya"

Fargabar samun matsalar cunkoso

A duk cikin shugabanin, shugaba Francois Hollande na Faransa kaɗai ya fito kai tsaye ya bayyana zuciyarsa yana mai cewa:

"Mene ne aikinmu? alhakinmu ne mu tabbatar cewa waɗannan mutanen sun sami kyakyawar makoma a ƙasashensu na asali. Ba wai bayar da mafaka ga duk waɗanda suka ƙetara suka zo Tuari ba ne abin da ya dace, wannan tamkar mafarki ne, zaku iya tunanin irin matsin lambar da wannan zai janyo, idan kuka yi la'akari da irin abubuwan da wasu ƙasashenmu ke fiskanta yanzu"

Ko a sauran ƙasashen Turan, akwai ƙaruwar adawa da shigowar baƙi saboda haka, shugabanin na ganin cewa kaɗan nai zai sauya a dokokin da suka shafi siyasar 'yan gudun hijira. Yawancinsu na takaicin hatsarin jirgin ruwan da yayi sanadiyyar rayukan 'yan gudun hijira a kwanakin baya amma matakin da suke ganin ya dace a ɗauka shine tabbatar da tsaron waɗannan 'yan gudun hijira.

Mawallafa: Hasselbach Christoph/ Pinaɗo Abdu Waba
Edita: Umaru Aliyu

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani