1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron ƙasashen ƙungiyar haɗin kan larabawa

June 15, 2007
https://p.dw.com/p/BuIk

Yau ne ƙungiyar haɗin kann ƙasashen larabawa, ta fara zaman taro na mussamman a birnin Alƙahira na kasar Masar.

Mahimman batutuwa da ke ajendar wannan taro,sun haɗa da halin da ake ciki a Palestinu da kuma ƙasar Libanon.

Praministan Fouad Siniora na Libanon, ya gayyaci taron bayan kisssan gilar da a ka yiwa ɗan majalisar dokoki Walid Eido, ranar lataba da ta gabata.

Sannan ƙasashen larabawan za su mahaura a game da adawar ƙasar Syria, a kann batun kotun ƙasa da ƙasa da Majalisar Ɗinkin Dunia ta girka ,domin sharia´ar kisan tsofan Pamninstan Libanon Rafi Hariri.

Kazalika , taronzai duba, rikicin da ake cigaba da gwabzawa, tsakanin dakarun ƙasar Libanon, da yan takifen ƙungiyar Palestinawa ta Fath Al-Islam.

Hukumomin Libanon sun zargi Syria, da hannu a cikin wannan rikici , zargin da Damascus ta mussanta.

Masu kula al´ammura a yankin gabas ta tsakiya, sun hango cewar, taron na Alƙahira ba zai tsinana kamai ba, ta la´akari da mummuna rabuwar kanu, tsakanin ƙasashen larabawa, a game da batutuwan da tawagogin za su tantana akai.