1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tarayyar Afirka ta bukaci kyale 'yan agaji yankin Habasha

Suleiman Babayo LMJ
September 3, 2021

Kungiyar Tarayyar Afirka ta bukaci gwamnatin Habasha tatabbatar kungiyoyin agaji jinkai sun kai yankin Tigray mai fama da rikici.

https://p.dw.com/p/3ztaf
Tigray Konflikt | Äthiopien Eritrea Flüchtlinge
Hoto: GIULIA PARAVICINI/REUTERS

Kungiyar Tarayyar Afirka ta bukaci gwamnatin Habasha ta dauki matakan tabbatar da cewa kungiyoyin jinkai sun samu shiga yankin Tigray domin kare mutane daga matsanancin yunwa, sakamakon rikicin da ke faruwa a wannan yankin.

Yankunan arewacin kasar sun fada cikin rikici a watan Nowamba da ya gabata lokacin da gwamnatin Firaminista Abiy Ahmed ya tura sojojin da suka kawo karshen gwamnatin yankin na Tigray karkashin TPLF, sakamakon harin da aka kai kan sansanin sojojin gwamnatin tarayya a yankin. Akwai zargin duk bangarorin da ke rikici na kasar ta Habasha ana zargi da cin zarafin fararen hula.