1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tallafin Turai ga warware rikicin Mali

Umar Saleh SalehNovember 19, 2012

EU ta nuna goyon baya ga shirin tallafawa Mali domin murƙushe 'yan tawaye.

https://p.dw.com/p/16m0J
In this Thursday, Sept. 27, 2012 photo, Islamist commanders instruct 13-year-old fighter Abdullahi to man a pickup-mounted machine gun, during a meeting with an AP journalist, in Douentza, Mali. Islamists in northern Mali have recruited and paid for as many as 1,000 children from rural towns and villages devastated by poverty and hunger. The Associated Press spoke with four children and conducted several dozen interviews with residents and human rights officials. The interviews provide evidence that a new generation in what was long a moderate and stable Muslim nation is becoming radicalized, as the Islamists gather forces to fight a potential military intervention backed by the United Nations. (Foto:Baba Ahmed/AP/dapd)
Hoto: AP

Ministocin kula da harkokin ƙasashen ƙungiyar tarayyar Turai sun yi marhabin lale ga shirye-shiryen taimakawa shirin bayar da horo ga dakarun ƙasar Mali da nufin kawar da mayaƙan da suka karɓe iko da yankin arewacin ƙasar. Ƙasashe mambobin ƙungiyar ta EU, waɗanda suka gudanar da taron su a birnin Brussels, da ke zama cibiyar ƙungiyar tarayyar Turai - a wannan Litinin, sun amince da ƙoƙarin sake fasalin rundunar sojin ta Mali, tare da yin ƙira ga hanzarta kammala shirin domin amincewa da shi - nan da watan Disamba.

Tunda farko dai gwamnatin wucin gadin ƙasar ta Mali ta buƙaci samun tallafin ƙetare, inda ƙungiyar cinikayya ta yankin yammacin Afirka, ta ECOWAS da kuma Majalisar Ɗinkin Duniya ke haɗa hannu wajen tsara rundunar kiyaye zaman lafiya a ƙasar.

Ministocin ƙasashen Turai ɗin dai suka ce akwai buƙatar fayyace wurin da zai kasance cibiyar rundunar - daga cikin ƙasashen da ke makwabtaka da ita Malin, da kuma buƙatar bada kariya ga sojojin Turai da ke bayar da horo ga dakarun na ƙasar Mali. Akan hakane, taron ministocin na EU ya buƙaci ƙasashe mambobi da su bayar da gudummowar su ga shirin.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Usman Shehu Usman