1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Takaddama kan tafiya aikin Hajji

September 10, 2013

Kamfanonin Hajji da Umrah a Nijar sun koka dangane da karin kudade da gwamnatin kasar ke shirin dora wa kowane maniyaci na kasar.

https://p.dw.com/p/19fdi
Source News Feed: EMEA Picture Service ,Germany Picture Service An aerial view shows Muslim pilgrims circling the Kaaba and praying at the Grand mosque on the second day of Eid al-Adha in Mina, near the holy city of Mecca October 27, 2012. Muslims around the world celebrate Eid al-Adha to mark the end of the Haj by slaughtering sheep, goats, cows and camels to commemorate Prophet Abraham's willingness to sacrifice his son Ismail on God's command. REUTERS/Amr Abdallah Dalsh (SAUDI ARABIA - Tags: RELIGION SOCIETY)
Hoto: Reuters

A daidai lokacin da ya rage 'yan kwanaki kalilan a soma jigilar maniyatan kasar ta Nijar zuwa kasar Saudiyya domin sauke faralin bana kamfanonin Hajji da Umrah na kasar sun koka dangane da wani mataki da gwamnati ta dauka na karbar wasu kudade sama da jikka dari na CFA ga kowane maniyaci domin abinci a wurin
kwaciya.

Wanann ya zo ne kwana daya bayan da wasu kungiyoyi suka yi zargin cin hanci wajan bayar da kwangilar jigilar maniyatan da kuma tsauwala farashin kudin jirgi.

To sai dai a wani taron manema labarai da ta kira a ranar Talata hukumar koli mai kula da aikin Hajji da Umrah a kasar ta Nijar wato COHO ta mayar da martani a kan wadannan zarge-zarge da ake yi mata.

Shirye-shiryen fara jigilar maniyata

Da ya ke jawabi a gaban manema labarai shugaban hukumar ta COHO Alhaji Bello Garba ya ce ya zuwa yanzu shirye-shiryen jigilar maniyatan komi na tafiya daidai musamman dangane da batun bisa, sun cimma wani shiri da hukumomin Saudiyya inda kowa zai samu tashi bisar ba tare da wahala ba. Kana kuma kudin kujera zai tashi jikka 950 sabanin 980 a bara. Ya kara da cewa jirgin farko zai tashi ne ranar 15 ga wanann wata na Satumba.

MEDINA, SAUDI ARABIA: The Prophet Mohammed's Mosque is lite for sunset prayer in Medina 24 January 2004. The Prophet Mohammed is buried in the mosque and it is second most holy site of Islam. Two million Muslims are expected to make the pilgrimage to Mecca in the coming days.
Masallacin Annabi (SAW) a MadinaHoto: Getty Images

A baya dai wasu kungiyoyin farar hula sun zargi hukumar da cewa ta hada baki da kamfanin Max Air na Dahiru Mangal domin kwace kason kujerun wasu kamfanonin da suka samu izinin jigilar maniyatan kasar da ma daga farashin
kujerar daga jikka 905 da aka cimma a baya zuwa 950.
Sai dai ko baya ga wadannan korafe-korafe lokacin wani taron manema labarai da suka kira a ranar Talata, kawancan kamfanonin Hajji da Umrah na BAB Makka sun nuna damuwarsu da wani mataki da hukumar ta dauka na karbar wasu kudade sama da jikka dari ga maniyatan da sunan abinci da gurin kwanciya.

Mawallafi: Gazali Abdu Tasawa

Edita: Mohammad Nasiru Awal

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani