1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Takaddama a kan sabon kasafin kudin Amirka

October 5, 2013

Sakataren harkokin wajen Amirka ya ce rufe harkokin gwamnatin Amirka zai raunana matsayinta a idon duniya.

https://p.dw.com/p/19uAt
Furloughed federal workers join a rally with Congressional Progressive Caucus to demand a vote to end the government shutdown, outside the U.S. Capitol in Washington, October 4, 2013. House Republicans held their ground on Friday in a standoff with President Barack Obama over the U.S. government shutdown, accusing him of intransigence and not caring about the impact on the American people as the crisis dragged into a fourth day. REUTERS/Jonathan Ernst (UNITED STATES - Tags: POLITICS BUSINESS HEALTH EMPLOYMENT) - eingestellt von gri
Hoto: Reuters

Sakataren kula da harkokin wajen Amirka John Kerry, ya yi gargadin cewar, tsawaita lokacin takaddamar siyasar da ta barke a kasar, ka iya raunana matsayin Amirka a idon duniya, yayin da matakin rufe harkokin gwamnatin Amirka ya shiga yininsa na biyar kenan a jere. Kerry, ya ambata a wajen taron hadin kan tattalin arziki na kasashen yankin Asiya da Pacific da ke gudana a Bali na kasar Indonisiya cewar, tsawaita lokacin takaddamar, ko kuma maimaita ta, zai sa mutane su fara aza ayar tambayar ko ma Amirka za ta iya zama abar misali ga sauran kasashen, wanda kuma ya ce yana fatan ba za a kai ga wannan yanayi ba.

A halin da a ke ciki kuma, shugaba Amirka Barak Obama ya soke ziyarar da ya shirya kai wa Asiya da kuma wasu manyan tarukan kasa da kasa guda biyu, saboda dakatar da ayyukan gwamnatin Amirka sakamakon takaddama a tsakanin majalisun dokokin kasar a kan kasafin kudi.

Tun dai ranar Talatar da ta gabata (01. 10. 13) ce, ayyukan hukumomi da ma'aikatun gwamnatin da ayyukansu bai zama tilas ba ya tsaya cik sakamakon gaza cimma daidaito a kan sabon kasafin kudin kasar. 'Yan jam'iyyar Republicans da ke da rinjaye a majalisar wakilai na neman shugaba Obama ya jinginar da shirin samar da sauye sauye a sashen kula da lafiyar da yake neman yi, ko kuma hana samar da kudi domin shirin. Ya zuwa yanzu kuma babu wata alamar cewar, takaddama tsakanin majalisar wakilai da ta dattijai a kan batun, ta kusa kawo karshe.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Mohammad Nasir Awal