1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Bala'i

Jamhuriyar Nijar ta amince da dokar kariya kan bala'i

Suleiman Babayo
December 6, 2018

Jamhuriyar Nijar ta amince da dokar kariya ga mutanen da suka tsere daga bala'i.

https://p.dw.com/p/39cLW
DW - Global 3000 - Niger Flucht
Hoto: ZDF

Jamhuriyar Nijar ta zama kasa ta farko a nahiyar Afirka da ta amince da shiri na kasa kan kariya da taimakon mutanen da suka tsere daga wuraren da ake samun tashe-tashen hankula da ambaliyar ruwa da fari.

Majalisar Dinkin Duniya da gwamnatin kasar suka tabbatar da haka a wannan Alhamis. Lawan Magagi ministan lamuran jinkai na kasar ya ce kimanin mutane 174,000 suka tsere zuwa kasar ta Jamhuriyar Nijar galibi daga Najeriya da Mali sakamakon rikicin kungiyoyin masu matsanancin kishin addinin Islama. Akwai wasu kasashen da suka amince da wannan kudirin dokar na shekara ta 2009 na Tarayyar Afirka, amma ba su saka cikin dokokinsu ba tukunna.