1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sulhu a tsakanin Isra'ila da Falasdinu

August 21, 2013

Isra'ila ta ce za ta yanke wasu shawarwari masu ban mamaki a tattaunawarta da Falasdinu.

https://p.dw.com/p/19Tpe
COMBINATION PICTURE - (FILES) - A file picture dated 30 November 2011 show the the head of Israel's parliamentary opposition Tzipi Livni (L) during a news conference at the Knesset, in Jerusalem, Israel. Another file picture dated 26 May 2013 shows Palestinian Chief negotiator Saeb Erekat at the second day of World Economic Forum, Dead Sea, west of Amman, Jordan. EPA/ABIR SULTAN/Jamal Nasrallah (Zu dpa "Israelis und Palästinenser nehmen direkte Friedensgespräche auf")
Hoto: picture-alliance/dpa

Bayan gudanar da wani zagaye na tattaunawa a tsakanin Falasdinu da Isra'ila a wannan Talatar (20.08.13), kuma duk da cewar daukacin sassan biyu sun yi alkawarin kin bayyanawa jama'a irin abubuwan da suka cimma, jagorar wakilan Isra'ila a wajen tattaunawar, kana ministar shari'ar kasar Tzipi Livni, ta sanar ta wata tashar rediyon Isra'ila cewar, kasar za ta yanke wasu muhimman shawarwari na ban mamaki domin cimma yarjejeniyar zaman lafiya ta karshe da Falasdinu. Ta kuma nuna takaicinta dangane da rashin samun goyon baya ga tataunawar, daga bangaren masu tsattsauran ra'ayin da ke cikin gwamnatin kawancen kasar, a karkashin fira minista Benjamin Netanyahu. Wannan tattaunawar dai, sakataren harkokin wajen Amirka John Kerry ne ya tsara, a karon farko cikin tsukin shekaru biyar. Dama tun a shekara ta 2008 ne, tattaunawar ta katse, sakamakon takaddama a kan batutuwan da suka hada da samar da karin matsugunai a yankunan da Falasdinawa ke fatan ya kasance kasarsu a nan gaba, wanda hukumomin na Isra'ila ke yi.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Umaru Aliyu