An karfafa tsaro bayan kisan mutum 290
April 22, 2019Talla
Rayuka 290 suka salwanta yayin da wasu fiye da 500 suka sami rauni a jerin hare-haren da aka kai kan coci-coci da otel-otel da suka jefa kasar cikin yanayi na jimami tare da fargabar barkewar rikici na kabilanci. Tuni ma dai rahotanni ke nuni da cewa an kai wasu hare-hare da ake ganin na ramuwar gayya ce a wani yanki da ke arewa maso yamma na kasar a daren ranar Lahadi.
A wannan Litinin shugaban kasar Mai-thri-pala Siri-sena ya kira wani taro na gaggawa da ya hada da kwamitin tsaro.
Kawo yanzu babu kungiyar da ta fito ta dauki alhakin kai wadannan hare-haren a yayin da mabiya addinin kirista kamar sauran kasashen duniya ke tsakiyar bikin Easter, daya daga cikin manyan bukukuwan mabiya wannan addini a duniya.