1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An karfafa tsaro bayan kisan mutum 290

Ramatu Garba Baba MNA
April 22, 2019

Wasu 'yan kunar bakin wake 7 ne suka kaddamar da hare-haren da suka lakume rayuka 290 a yayin da gwamnatin kasar ta janye dokar hana fita da ta sanya a birnin Colombo da ke cikin jimami a sanadiyyar ayyukan ta'addanci.

https://p.dw.com/p/3HClk
Sri Lanka Negombo Explosion in St. Sebastian Kirche
Hoto: Reuters/Stringer

Rayuka 290 suka salwanta yayin da wasu fiye da 500 suka sami rauni a jerin hare-haren da aka kai kan coci-coci da otel-otel da suka jefa kasar cikin yanayi na jimami tare da fargabar barkewar rikici na kabilanci. Tuni ma dai rahotanni ke nuni da cewa an kai wasu hare-hare da ake ganin na ramuwar gayya ce a wani yanki da ke arewa maso yamma na kasar a daren ranar Lahadi.

A wannan Litinin shugaban kasar Mai-thri-pala Siri-sena ya kira wani taro na gaggawa da ya hada da kwamitin tsaro.

Kawo yanzu babu kungiyar da ta fito ta dauki alhakin kai wadannan hare-haren a yayin da mabiya addinin kirista kamar sauran kasashen duniya ke tsakiyar bikin Easter, daya daga cikin manyan bukukuwan mabiya wannan addini a duniya.