Nijar: 'Yan ta'adda sun kashe sojoji
December 24, 2020Talla
Ma'aikatar tsaron Jamhuriyar Nijar ta sanar da mutuwar sojojin kasar bakwai a yayin wani kwantar baunar 'yan ta'adda a kauyen Tarun da ke arewacin Ouallam.
Sai dai sanawar da ma'aikatar tsaron kasar ta fitar, ta ce rundunar zaratan sojanta, ta samu nasarar hallaka mayakan jihadi 11 a yayin batakashin da 'yan ta'adda, da ya gudana a ranar Litinin a yankin Tillaberi mai fama da hare-haren kungiyar da ke da'awar jihadi.