1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Najeriya sun yi ikirarin kashe 'ya'yan Boko Haram 150

September 18, 2013

Wannan labari da ya fito a wannan Laraba ya ci karo da ikirarin da Boko Haram ita ma ta yi cewa ta kashe sojoji 40 a wani kwantan bauna da ta yi wa rundunar ta Najeriya.

https://p.dw.com/p/19k6z
Nigerian soldiers patrol in the north of Borno state close to a Islamist extremist group Boko Haram former camp on June 5, 2013 near Maiduguri. Nigeria's military yesterday disclosed details of its offensive against Islamist militants, describing a series of events that saw insurgents take control of a remote area before being pushed out by soldiers. AFP PHOTO / Quentin Leboucher (Photo credit should read Quentin Leboucher/AFP/Getty Images)
Hoto: Quentin Leboucher/AFP/Getty Images

Rundunar sojin Najeriya ta fada a wannan Laraba cewa wani farmaki da sojojin kasar suka kai makon da ya gabata a kan wani sansanin Kungiyar nan da ake wa lakabi da Boko Haram, da ke arewa maso gabacin kasar ya yi sanadiyar mutuwar 'yan bindigar Islama 150 da sojoji 16. Sai dai wasu rahotanni sun ce sojoji 40 suka mutu a wani kwatan bauna da 'ya'yan Boko Haram suka yi wa wani gungun sojoji sannan wasu da dama sun bata. Sai dai babu wani jami'in sojin da ya yi karin bayani game da rahoton da ke cewa Boko Haram ta yi musu kwantan bauna, in ban da farmakin da rundunar ta ce ta kai a makon da ya gabata, wanda sai a wannan Laraba labarin ya fito fili. An jiyo kakakin soji Ibrahim Attahiru na cewa sansanin na 'yan kutse da ke cikin dajin Kasiya a jihar Borno na da girma kuma sun gano manyan makamai a ciki.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Umaru Aliyu