1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojoji sun hallaka kwamandan Boko Haram

Usman ShehuAugust 14, 2013

A Najeriya jami'an tsaron sun sanar da cewa sun hallaka mataimakin shugaban ƙungiyar Boko Haram, wato Momodu Bama

https://p.dw.com/p/19Q9Q
epa03701818 Nigerian soldiers fire rifles on a shooting range in Bauchi, Nigeria, 15 May 2013. Nigerian President Goodluck Jonathan (not pictured) on 14 May 2013 declared a state of emergency in three north-eastern Nigerian states hardest hit by the radical Islamist Boko Haram insurgency. More security forces would be deployed to these areas to flush out Islamist insurgents, but all political office holders in the three states would remain in office, Jonathan said on 14 May. EPA/DEJI YAKE +++(c) dpa - Bildfunk+++
Sojojin Najeriya a MaiduguriHoto: picture-alliance/dpa

Rundunar tabbatar da tsaro da zaman lafiya a Najeriya da aka sani da JTF, ta sanar da cewa ta samu nasarar hallaka Momodu Bama da ake wa laƙabi da Abu Saad, wanda babban kwamandan ƙungiyar Boko Haram wanda ke zama na biyu a karfin iko, bayan jagoran ƙungiyar Imam Abubakar Shekau. A wata sanarwar da kakakin rundunar Laftanar kanar Sagir Musa ya aikewa manema labarai, ya ce rundunar ta samu nasarar hallaka Momodu Bama a wani gumurzu da aka yi, yayinda jami'an tsaron ke kokarin magance wani hari da ‘yan ƙungiyar gwagwarmayar suka nemi kai wa a garin Bama a farkon watan nan. A cewar wakilinmu Amin Sulaiman Muhammad, Momodu Bama da ake yi wa laƙabi da Abu Saad yana cikin waɗanda kasar Amirka ta sanya makuɗan kuɗaɗe akan su, kuma babban na hannun daman jagoran kungiyar ne. Babu dai wata kafa mai zaman kanta da ta tabbatar da ikirarin jami'an tsaron.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita:        Saleh Umar Saleh