Shugabannin Afirka masu dogon zamani
Wasu shugabannin Afirka na kan mulkli tun da dadewa wanda yawancin ‘yan kasar ba su san wani shugaban ba. Daya daga cikin mafi dadewan shi ne Paul Biya na kasar Kamaru da ke neman wani sabon wa’adi na shekaru bakwai.
Shugaban Kamaru: Paul Biya
Paul Biya mai shekaru 85, na daga cikin shugabanni mafi dadewa a Afirka. Yana rike da mulki tun a shekara ta 1982. Shugaban Equatorial Guinea shi kadai ya fi shi dadewa. A ranar bakwai ga watan Oktoba na shekara ta 2018 zai tsaya takara a wani sabon wa’adi na bakwai. A shekara ta 2008 aka yi wa kundin tsarin mulkin Kamaru kwaskwarima ta musammun domin bai wa Biya damar ci gaba da mulki.
Äquatorialguinea: Teodoro Obiang Nguema
Teodoro Obian Nguema a yanzu shi ne shugaba mafi dadewa a Afirka. Ana matukar adawa da shi. Shi ne ke kan gaba a cikin shugabannin Afirka masu dogon zamani. A shekara ta 2017 Shugaban Kasar Angola, José Eduardo dos Santos ya bar mulki bayan da ya karbi ragamar tun a shekara ta 1979, kamar yadda shi ma Nguema, Obiang ya sanar a shekara ta 2016 cewa ba zai yi takara ba a shekara ta 2020.
Shugaban kasar Aljeriya: Abdelaziz Bouteflika
Abdelaziz Bouteflika dan shekaru 81 ya kwashe shkearu 19 yana mulki. Bayanai na nuna cewar zai sake tsayawa takara a zaben shugaban kasa na shekara ta 2019. Hakan duk da cewar shugaban na Aljeriya na fama da rashin lafiya tun a shekara ta 2013, kuma babu wasu alamun da ke nuna cewar ba zai tsaya takara ba.
Shugaban kasar Yuganda: Yoweri Museveni
Yoweri Museveni yana kan mulki kusan shekaru 30 da suka wuce. Yawancin ‘yan kasar ba su san wani shugaba ba sai shi ba. Kishi 75 cikin dari na ‘yan Yuganda miliyan 35 an haifesu ne bayan ya fara mulki a shekara ta 1986. A shekara ta 2017, Museveni ya amince da wata doka wacce ta cire kayyade shekaru kafin tsayawa takara a zaben shugaban kasa. A yanzu a shekara ta 2021 zai iya yin takara.
Shugaban Kasar Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango: Joseph Kabila
Joseph Kabila ya gaji mahaifinsa a shekara ta 2001 a matsayin shugaban Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango. A shekara ta 2016 wa’adin mulkinsa na biyu ya kammala. Kabila ya ci gaba da kafewa a kan mulki, tare da kawo jinkiri wajen gudanar da zaben wanda zai maye gurbinsa. Za a zabe shi a zaben ranar 23 ga watan Disamba na shekara ta 2018. Ko da yake ma Kabila ya ce ba zai sake yin takara ba.
Shugaban Jamhuriyar Kwango: Denis Sassou Nguesso
Wani gyaran fuska na kudin tsarin mulki ne ya bai wa Denis Sassou Nguesso damar sake tsayawa takara a shekara ta 2016 tare kuma da samun nasara a zaben na Jamhuriyar Kwango. Denis Sassou Nguesso na kan karagar mulki tun shekaru 30, ko da yake ma ya dan dakata tsakanin shekara ta 1992 zuwa 1997.
Shugaban kasar Ruwanda: Paul Kagame
Paul Kagame na a kan mulkin Ruwanda tun a shekarun 2000. A wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a da ya shirya a shekara ta 2015, an amince da yi wa kudin tsarin mulkin sauye-sauye. Wanda kundin ya bai wa shugaba damar yin wa’adi biyu kawai na mulki. A shekara ta 2017 Paul Kagame ya sake takara kuma zai iya ci gaba da mulki har ya zuwa shekara ta 2034, idan har ya samu nasara a zaben shugaban kasa.
Shugaban kasar Burundi: Pierre Nkurunziza
A shekarar 2005 Pierre Nkurunziza ya karbi mulki. Takararsa ta wa’adin mulki na uku ta janyo yamutsi a shekara ta 2015. Kimanin mutane 1200 suka mutu kana sama da dubu 400 suka bar gidajensu. A cikin watan Mayu na shekara ta 2018, an gudanar da wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a don yin gyaran fuska ga kundin tsarin mulki. Tun lokacin wa’adin mulkin shugaba ya koma shekaru bakwai.
Shugaban kasar Gabon: Ali Bongo Ondimba
Ali Bongo har yanzu bai kai yawan shekarun da mahaifinsa ya yi a kan mulki ba. Mahaifin nasa ya yi mulkin shekaru 41 ne. Ali Bongo ya zama shugaban kasa bayan nasarar da ya samu a zaben shekara ta 2017, a wa’adi na uku na mulki. A shekara ta 2018 aka yi wa kudin tsarin mulkin kasar kwaskwarima wanda ya kara bai wa shugaban kasar cikakken iko.
Shugaban kasarTogo: Faure Gnassingbé
A shekarun 2005 Faure Gnassingbé ya karbi mulki bayan mutuwar mahaifinsa wanda ya yi shekaru 38 a kan karaga. Duk da zanga-zangar da jama’a suka yi ta yi na nuna adawa da ci gaban mulkin zuri’ar Gnassinbe. A shekara ta 2017 aka amince da wata doka ta kayyade wa’adin mulki na shugaban kasa, sai dai shugaban da ke barin gado dokar ba ta shafe shi ba, zai kuma tsaya takara a zaben shekara ta 2020.