1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Indonesiya ya sanar da abokin takararsa

Zulaiha Abubakar MNA
August 9, 2018

Shugaba Joko Widodo na kasar Indonesiya ya bayyana zaben Ma'ruf Amin shugaban majalisar malaman kasar a matsayin wanda za su yi takara tare a zaben kasar mai zuwa.

https://p.dw.com/p/32tbn
Joko Widodo
Joko WidodoHoto: Reuters/Beawiharta

Shugaba Joko Widodo ya ce Ma'ruf Amin mai shekaru 75 da haihuwa wayayyen malamin addinin Islama ne, sannan dukkanin jam'iyyu tara da suka yi hadaka sun amince da zabin nasa. A ranar Juma'a shugaba Widodo da Amin za su yi rijista a hukumar zaben kasar.

Kasar Indonesiya wacce ta kasance daya daga cikin kasashen duniya masu yawan Musulmi za ta gudanar da zabe a watan Afrilun shekara ta 2019.

Har yanzu dai babu wani raddi game da batun zabo Ma'ruf Amin daga bangaren mataimakin shugaban kasar Muhammad Yussuf Kalla, wanda ya kasance mutum na farko a kasar da ya yi mataimakin shugaban kasa sau biyu.