1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban kasar Bama ya yi murabus

Gazali Abdou Tasawa
March 21, 2018

Shugaban kasar Myanmar ko Bama Htin Kyaw ya sanar a wannan Laraba da yin murabus daga kan mukaminsa na shugaban kasa. Ya sanar da wannan mataki nasa ne a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na facebook. 

https://p.dw.com/p/2ufZs
Myanmar  Präsident Htin Kyaw
Hoto: Reuters/D. Sagolj

Babu dai wani bayani da shugaban ya bayar a game da dalillansa na yin murabus din, sai dai kafofin yada labaran kasar da dama sun danganta matakin da tarbarbarewar yanayin lafiyar jikin shugaban. 

A watan Aprilun shekara ta 2016 ne Shugaban wanda ke daya daga cikin abokanan gwagwarmayar Aung San Suu Kyi a shekarun baya, ya karbi ragamar mulkin kasar ta Myanmar ko Bama inda ya zamo shugaban farar hula na farko a cikin gwamman shekaru na baya-bayan nan na tarihin kasar. Sanarwar fadar shugaban kasar ta bayyana cewa za a nada sabon shugaban kasa a cikin mako daya daga yanzu.

Majalisar Dinkin Duniya dai na zargin gwamnatin kasar ta Bama da aikata kisan kiyashi kan al'ummar tsirarun Musulmin kasar 'yan kabilar Rahongyas wadanda yanzu haka sama da dubu 70 suka tsere zuwa makobciyar kasarsu ta kasar Bangladesh domin tsira da rayukansu daga kisan da suke fuskanta a kasar.