1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaba Assad ya ce ba zai gabatar da kansa ga masu bincike ba

January 21, 2006
https://p.dw.com/p/BvBJ

A lokacin da yake ambaton ´yancin Syria, shugaba Bashar al-Assad ya ce ba zai gabatar da kansa don amsa tambayoyi daga jami´an MDD dake bincike kisan gillar da aka yiwa tsohon FM Libanon Rafik Hariri ba. A wani jawabi da yayiwa kungiyar lauyoyin Larabawa Assad ya ce duk da haka zai ci-gaba da ba da hadin kai ga binciken da kasashen duniya ke yi. Assad ya ce batun kare ´yancin Syria shi ne mafifici akan duk wani bincike na MDD. Jami´an MDD sun ce Syria ba ta ba da hadin kai yadda ya kamata. Tsohon shugaban masu binciken kuma mai shigar da kara na Jamus Detlev Mehlis ya zargi manyan jami´an leken asirin Syria da na Libanon da hannu a kisan da aka yiwa Mista Hariri a cikin watan fabrairun bara.