1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shirye-shiryen zaben shugaban kasa a Ghana

Mohammad AwalDecember 6, 2012

A nahiyar Afrika,Ghana ce kasa daya tillo da ta yi fuce gurin shirya zabubuka mafi tsbata. Abun da ke daya daga cikin dalillan da suka sa Obama ya kai ziyara a kasar.

https://p.dw.com/p/16wdA
A woman casts her ballot during presidential elections in Accra, Ghana, Sunday Dec. 28, 2008. Ghanaians returned to the polls Sunday for a presidential runoff vote with Nana Akufo-Addo of the ruling party facing opposition candidate John Atta Mills in an election expected to further solidify the country's status as one of Africa's few stable democracies.(AP Photo)
Hoto: AP

Ana kwatanta kasar Ghana a matsayin kasa dake kan gaba wajen bin tafarkin demokradiyya da ma kwanciyar hankali a Nahiyar Afrika dangane da kwazo da himma, game da kwatanta gaskiya da take aiki da shi wajen ganin cewar demokradiya ta samu karbuwa a kasar. Tun sanda kasar ta fara bin tsarin demokradiyya a shekara 1992 dai ta gudanar da zabuka biyar, ko da shike ta fuskanci wasu kalubale da dama, amma dai bata yi kasa a gwiwa ba domin kuwa ta cigaba da samar da dawamamiyar zaman lafiya a sassa daban daban na kasar.

Duba yadda aka tafiyar da yakin neman zabe ya zuwa wannan lokacin ko shakka babu wannan zaben dake tafe kasa da saoi 24, za'a gudanar dashi bisa darussan da kasar ta koya a zabukan da suka gabata da ma wadanda aka gudanar a wasu kasashen duniya ta hanyar rungumar tsarin yin anfani da na'urar Computer.
A ranar talatar da ta gabata dai hukumar zabe ta shirya wa maaikatar tsaron kasar zabe na musamman dayake sune za su kula da tabbatar da cewar an samar da kwanciyar hankali a duk runfunar zaben kasar.
Halin Dattako da kwanciyar hankali a yayin zaben ya baiwa kasar daraja a duniya.

Ghana Wahlkampf John Mahama
Shugaba John MahamaHoto: Getty Images

A gurin zaben, an fuskanci kalubale da dama kama daga tafiyar hawainiya da naurar keyi da rashin ganin sunayen wasu jamian tsaro a cikin rejista da dai sauransu, hakan dai ya sa jami'in hulda da jama'a na hukumar zabe mai zaman kanta Sylvia Annor ta yiwa jama'a bayani game da dalilin afkuwar haka:

Tace wasu yan tsaron da ba gano sunayensu a rufunan zaben da suka je kada kuria ba, ba daga nan ne suka rubuta sunayensu tun da farko ba. Misali wani da ya rubuta sunansa a jihar yamma, sai ga shi a osu dake jihar greater Accra wai zai kada kuria, ai hakan ba zai yiwu ba kuma ba taba yin haka ba sai da izini.
Duk da hakan dai shugaban hukumar zabe mai zaman kanta yace – hukumar - a shirye take da ta gudanar da wannnan zaben cikin kwanciyar hankali tare kuma da wanke kanta daga zargin da jamaa keyi cewar za ta iya tabka magudi:

Opposition presidential candidate Nana Akufo-Addo, center, looks on from the stage during his final campaign rally ahead of Friday's presidential election, in Accra, Ghana, Wednesday, Dec. 5, 2012. Far right is former Ghana President John Agyekum Kufuor. After five coups and decades of stagnation, the West African nation of 25 million is now a pacesetter for the continent's efforts to become democratic. Ghanaians will go to the polls on Friday to choose between four candidates, including President John Dramani Mahama, a former vice president who assumed the top post in July after the death of president John Atta Mills, and former foreign minister Akufo-Addo who lost the presidency by less than 1 percent in 2008.(Foto:Christian Thompson/AP/dapd)
Dan takarar NPP Nana Akufo-AddoHoto: dapd

"A shirye muke mu gudanar da wannan zabe kuma zabe na musamman da muka shirya na nuna cewar muna da na'urorin aiwatar da wannan aiki. ina mai tabbattar muku cewar zai yi wuya a tabka magudi a zaben nan kamar yadda wasu ke zato domin gabannin sakamakon zaben ya kai gare ni sai wakilan jam'iyyun siyasar sun amince kuma sun sanya hannu kana ni ma in sanya hannu sai in mika wa kungiya 'yan jaridu ta kasa. kenan zan zama mahaukaci idan na yiwa wannan sakamakon kwaskwarima."

A halin yanzu dai kasar na dauke da baki dabam dabam daga kasashen ketare da zasu sa ido akan wannan zaben, bayan kawo karshen yakin neman zabe a wannan Larabar.

Mawallafa: Rahmatu Abubakar/ Issoufou Mamane
Edita: Mohammad Nasiru Awal