A cikin shirin za a ji cewar Shugaban kasar Ghana Nana Akuffo Addo ya dauki alwashin ginawa mabiya Addinin Kirista wata babar Majami'a a kasar ,batun da a halin yanzu ya janyo cece-kuce tsakanin al'ummar kasar. Za kuma a ji cewar Jamusawa wadanda suka tsaya wa 'yan gudun hijira za su fuskanci tara ta dubban Euro.