A cikin shirin za ku ji cewar yayin da al'umma a Jamhuriyar Dimuradiyyar Kwango ke ci gaba da ka'da kuri'unsu, mazauna yankunan Beni da Butembo dake fama da cutar Ebola na gudanar da zanga-zanga sakamakon dage ranar zabe da hukumar zaben kasar tayi a wadannan yankuna.