MA
October 12, 2018Talla
Cutar kansa ta mama da kan kama mata, wata cuta ce da ke illa ga mata a sassa dabam-dabam na duniya ciki kuwa har da Najeriya. A kan haka masana da kwararrun likitoci suka tashi haikan don sama wa al'umma mafita.
A baya dai ana ganin tana kama mata ne da shekarunsu na haihuwa suka haura hamsin, sai dai a wannan lokaci lamarin na sauyawa saboda ana samun mata matasa masu kananan shekaru da cutar.
A jihar Kano da ke yankin arewa maso yammacin Najeriya, Dakta Maimuna Abdulkareem Halliru likita a asibitin kwarraru na Muhammad Abdullahi Wase, ta zurfafa bincike kan wannan cuta da sannu a hankali ke illa ga mata a jihar ta Kano.