1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sha'anin tsaro a Mali bayan nasara akan 'yan tawaye

January 31, 2013

EU ta nemi dakarun Afirka su hanzarta karbar alhakin tsaro a Mali daga hannun Faransa.

https://p.dw.com/p/17VMS
GettyImages 160414414 Slovenia Foreign Affairs minister Karl Erjavec and EU commissioner for International Cooperation, Humanitarian Aid and Crisis Response Kristalina Georgieva and High Representative of the European Union for Foreign Affairs and Security Policy Catherine Ashton (LtR) talk prior to a Foreign Affairs Council on January 31, 2013 at the EU Headquarters in Brussels. The Council will discuss the situation in the EU's southern neighbourhood, in particular in Syria and Egypt, and will prepare the forthcoming European Council debate on the Arab Spring. Ministers will also discuss the priorities of the foreign policy of the new US administration.They will be informed of the situation in Mali and the action taken by the EU in response to the special session of the last Foreign Affairs Council devoted to Mali. AFP PHOTO GEORGES GOBET (Photo credit should read GEORGES GOBET/AFP/Getty Images)
Hoto: AFP/Getty Images

Ministocin kula da harkokin wajen kasashen kungiyar tarayyar Turai, wadanda suka gana a wannan Alhamis, sun bukaci dakarun kasashen Afirka su hanzarta karbar ragamar kula da harkokin tsaro a kasar Mali, ba tare da wani bata lokaci ba.

Ministan kula da harkokin wajen Beljiam, Didier Reynders, wanda kasarsa ta kudiri anniyar ci gaba da tallafawa Faransa a irin matakan sojin da take dauka a kasar Mali - har ya zuwa ranar daya ga watan Maris, ya ce Turai na fatan cewar, nan bada dadewa ba, samame a kasar ta Mali, zai kasance wani alhaki ne daya rataya a wuyan daukacin kasashen duniya, wanda kuma zai sami goyon bayan Majalisar Dinkin Duniya, yana mai cewar musamman ma aikin zai kunshi sojojin kasashen yankin ne.

Shi kuwa ministan kula da harkokin wajen Jamus Guido Westerwelle, cewa ya yi abu mafi a'ala a yanzu shi ne kyalewa dakarun Afirka su jagoranci harkokin tsaron, wanda ya ce zai zama sauki ne ga ita kanta Faransa.

Sai dai takwaran aikinsa na Austria Michael Spindelegger, ya yi gagadin cewar mika harkokin tsaron ga dakarun Mali, ba mai yiwuwa bane anan kusa.

Nan gaba a wannan Alhamis ne ministan wajen Faransa Laurent Fabius, zai yiwa takwarorin aikinsa na kasashen Turai 27 jawabi dangane da ci gaban da aka samu a kasar ta Mali.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Umaru Aliyu