1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Senegal ta ba wa hambararren shugaban Guinea-Bissau mafaka

Abdoulaye Mamane Amadou
November 28, 2025

Hambararren shugaban kasar Guinea-Bissau Umaro Sissoco Embalo, ya isa a kasar Senegal inda zai ci gaba da samun mafaka bayan an masa juyin mulki.

https://p.dw.com/p/54PjY
Umaro Mokhtar Sissoco Embalo hamabararren shugaban kasar Guinea-Bissau
Umaro Mokhtar Sissoco Embalo hamabararren shugaban kasar Guinea-BissauHoto: Yonhap/YONHAPNEWS AGENCY/picture alliance

Hukumomi a Senegal sun tabbatar da isar hambararren shugaban kasar Guinea-Bissau Umaro Sissoco Embalo, inda zai ci gaba da samun mafakar siyasa bayan kifar da gwamnatinsa.

Juyin mulki a kasar Guinea-Bissau

Ma'aikatar harkokin wajen Senegal ce ta tabbatar da isar Mista Embalo a kasar, inda ta ce ya sauka Dakar, a cikin aminci da koshin lafiya, bayan ta aike da wani jirgin ya dauko shi daga Bissau babban birnin kasar Guinea.

Sojoji sun hambarar da gwamnati a Guinea-Bissau

Duk da duniya na suka da caccakar juyin mulkin ciki har da Majalisar Dinkin Dunia da ta bukaci a dawo kan turbar dimukuradiyya cikin gaggawa, sabon madugun juyin mulkin kasar Janar Horta N'Tam, ya karbi ranstuwar kama aiki, inda ya bayyan cewa zai jagoranci gwamnatin rikon kwarya ta shekara guda.

Kura ta lafa a Guinea-Bissau bayan juyin mulki

Tuni jam'iyyar adawa sun ki amincewa da juyin mulkin, suna mai bayyana hakan a matsayin wata kullalliya don hana tabbatar da sakamakon zaben da ya ba su nasara, suna masu kira da a gaggaua mika musu mulki.