Sassou-Nguesso na kan gaba a zaben Kwango
March 22, 2021Talla
Sakamakon tuni hukumar zaben kasar ta fara sanarwa na nuna cewa shugaba Sassou-Nguesso na kan gaba a gomman gundumomi, inda tuni ya samu nasarar kashi 85% a wasu gundumomi hudu. Shugaban mai ci a yanzu na neman karin waa'din shugabanci na hudu a kasar bayan shafe shekaru 36 a mulki.
Ranar Laraba ne hukumar zaben Kwango Brazavile za ta sanar da cikakken sakamakon zaben shugaban kasa. Amma 'yan adawa da kungiyoyin farar hula sun zargin bangaren gwamnati da aringizon kuri'u, tare da bayyana hukumar zaben kasar a matsayin 'yan korar gwamnati.