1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sakamakon zaɓen yan majalisun dokoki

July 5, 2012

Jam'iyyun siyasar da ke goyon bayan shugaban ƙasar Senegal Macky Sall sun sami rinjaye a zaɓen yan majalisun dokoki

https://p.dw.com/p/15RT5
Senegalese opposition presidential candidate Macky Sall (R) celebrates at a news conference in Dakar March 25, 2012. Senegal's long-serving leader Abdoulaye Wade admitted defeat in the presidential election, congratulating his rival Sall, a move seen as bolstering the West African state's democratic credentials in a region fraught with political chaos. REUTERS/Joe Penney (SENEGAL - Tags: POLITICS ELECTIONS PROFILE)
Hoto: Reuters

Ƙawancen jam'iyyun siyasar da ke goyon bayan shugaban ƙasar Senegal Macky Sall sun samu gagarumar nasara a zaɓen yan majalisun dokokin da aka gudanar a ƙarshen makon jiya.

Sakamakon wucin gadi da hukumar zaɓen ta baiyana, ya nuna cewar ƙawancen jam'iyyun sun samu kujeru 119 cikin 150 da ake da su a majalisar.Da yake baiyana sakamakon shugaban hukumar Demba Kandji ya ce jam'iyar tsohon shugaban ƙasar ta PDS wato Abdullahi Wade; ta samu kujeru 12,sanan wani ɗan aware na jam'iyar da ya kafa tasa jam'iyar ya samu wakilai 4 ,kana kuma sauran kujeru guda 15 sun fada cikin hanu wasu sauran ƙananan jam'iyyun siyasar.Wannan rinjaye da ƙawance da ake kira da sunnan na Beno Bokk Yakar ya samu a majalisar,zai baiwa shugaba Macky Sall damar ƙaddamar da manufofin gwamnatin sa

Mawallafi: Abdourahamane Hassane
Edita : Mohammed Nasiru Auwal