1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rundunar Monusco za ta janye daga Kwango

April 2, 2014

Shugaban Rundunar Martin Kobler shi ne ya bayyana haka a wajen wani taron manema labarai da yi.

https://p.dw.com/p/1BaQ0
UNO-Mission Kongo
Hoto: DW/D. Köpp

Rundunar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Ɗinkin Duniya da ke a Jamhuriyar Demokradiyyar Kwango wato Monusco ta sanar da cewar za ta janye da sannu a hankali daga ƙasar bayan ta kwashe shekaru da dama tana aikin tabbatar da zaman lafiya. A wani taron manema labarai da ya yi a yau a birnin kinshasha, jagoran rundunar Martin Koblerdan asilin kasar Jamus, ya ce "tafiyar ba yau ba ne, ko gobe, ko jibi, ya ce zamu janye da sannu a hankali."

A cikin watan Disamba aka shirya babban sakataran Majalisar Ɗinkin Duniya Ban Ki Moon zai gabatar da ƙudirin janye rundunar. Bayan da dakarun suka yi nasara a kan ɓangarorin 'yan tawaye da dama da ke a gabashin Kwangon abin da ya sa aka samu kwanciyar hankali. Akwai dakaru kusan dubu 20 na Majalisar Ɗinkin Duniya da ke jibge a ƙasar ta Kwango.

Mawallafi: Abdourrahamane Hassane
Edita: Mohammad Nasiru Awal