1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rundunar JTF ta ce akwai nasara a yaƙi da Boko Haram

Usman ShehuJanuary 14, 2013

Rundunar wanzar da zaman Lafiya a Maiduguri ta sanar da akam wani babban kwamandan ƙungiyar Boko Haram

https://p.dw.com/p/17JZQ
This image taken from video posted by Boko Haram sympathizers shows the leader of the radical Islamist sect Imam Abubakar Shekau made available Wednesday Jan. 10, 2012. The video of Imam Abubakar Shekau cements his leadership in the sect known as Boko Haram. Analysts and diplomats say the sect has fractured over time, with a splinter group responsible for the majority of the assassinations and bombings carried out in its name. (AP Photo) THE ASSOCIATED PRESS CANNOT INDEPENDENTLY VERIFY THE CONTENT, DATE, LOCATION OR AUTHENTICITY OF THIS MATERIAL
Imam Abubakar Shekau, jagoran kungiyar Boko HaramHoto: AP

Rundunar tabbatar da tsaro da zaman lafiya a jihar Borno wacce aka fi sani da suna JTF ta bayyana cewa ta samu nasarar cafke wani babban kwamandan ƙungiyar Boko Haram mai suna Mohammed Zangina da aka fi sani da Mallam Abdullahi Alhaji Musa, wanda akansa rundunar ta sa kuɗi Naira miliyan 25 ga duk wanda ya kawo shi da rai ko a mace.

A cewar runudanar tabbatar da tsaro ta JTF Mohammed Zangina da aka fi sani da Mallam Abdullahi ko Alhaji Musa daya ne daga cikin manyan ‘yan majalisar koli da ake kira “Shura” ta Kungiyar gwagwarmayar, kuma yana da hannu a shirya yawancin hare-hare da aka kai a sassan kasar wanda kungiyar ta dauki alhakin kaiwa.

In this Wednesday, Sept. 28, 2011 photo, police officers armed with AK-47 rifles stand guard at sandbagged bunkers along a major road in Maiduguri, Nigeria. The radical sect Boko Haram, which in August 2011 bombed the United Nations headquarters in Nigeria, is the gravest security threat to Africa's most populous nation and is gaining prominence. A security agency crackdown, which human rights activists say has left innocent civilians dead, could be winning the insurgency even more supporters. (Foto:Sunday Alamba/AP/dapd)
Yan sanda masu yaki da Boko HaramHoto: dapd

Kakakin rundunar ta JTF Laftanar Kanar Sagir Musa ya bayyana cewa sun samu nasarar kama shi ne a Maiduguri bayan musayar wuta da aka yi, inda ya kara da cewa a baya ya sha tsallake kwanton ɓauna da aka yi a maboyar sa a garuruwan Jos da Zaria da Potiskum da Damaturu. Kame wannan kwamandan na zuwa sa'o'i 24 bayan da jami'an tsaron suka bayyana kame wani kwamandan ƙungiyar ta Ahlul Sunnan Li'dda'awati Wal Jihad da aka fi sani da Boko haram a gidan wani tsohon dan majalisar wakilai da ya fito daga jihar Borno.

Sai dai jama'a na bayyana shakku kan wannan kame da jami'an tsaro suka ce sun yi, don haka tambayi Isma'il Yunusa wanda aka fi sani da Malam Kaka daya daga cikin masu wannan shakku, inda ya bani dalilin sa kamar haka. A baya ma dai rundunar ta ayyana kame wasu manyan kwamnadojin yaki na wannan kungiya, amma har yanzu ba a kai ga bayyana su gaban al'umma ba, wannan a cewar Malam Ahmad Gombe da lauje cikin nadi in ba haka ba da an bayyana su.

Mohammed Yusuf, der Gründer Nigeria's Boko Haram islamistisch
Mohammed Yusuf, wanda ya kafa kungiyar Boko HaramHoto: Screenshot Youtube

A wata sabuwa kuma rundunar tabbatar da tsaro da wanzar da zaman lafiya a jihar Borno ta sake jaddada cewa boye ‘yan kungiyar Boko Haram da al'ummar jihar Borno ke yi da kuma rashin baiwa jami'an tsaro hadin kai, shine ke zama babban kalubale ga kokarin shawo kan matsalar rikicin. Kakakin rundunar Laftanar Kanar Sagir Musa wanda ya bayyana hakan yace ya zama dole al'umma su taimaka wa jami'an tsaron in dai ana son kawo karshen wannan tashin-tashina. Saboda haka ya shawarci al'ummar jihar da su fito su bayyana inda masu kai hare-haren ta hanyar bai wa jami'an tsaro hadin kai da bayanai da za su taimaka musu a ayyukan su.

Zerstörte Fahrzeuge nach Bombenangriffen auf Polizeigebäude am Abend des 24.2.2012 in Gombe / Nigeria. Zu diesen Angriffen bekannte sich die islamistische Terrorgruppe Boko HaramFoto: Al-Amin Mohammed (DW Korrespondent), 25.2.2012, Gombe / Nigeria
Ofishin yan sanda da harin bam ya rusa a GombeHoto: DW

Sai dai da wuya jama'a su bada hadin kai ga jami'an tsaron bisa hujjojin da al'umma ke bayarwa na rashin kyakkyawan dangantaka tsakanin al'umma da jami'an tsaro, kamar yadda Malam Kaka da Ahmadu Gombe suka bayyana min. To amma jami'an tsaron na musanta wannan zargi da al'umma ke yi, inda suke kara karfafa gwiwar su tare da bada tabbacin rufe asirin duk wanda ya taimaka musu.

Mawallafi: Al-Amin Sulaiman Muhammad

Edita: Usman Shehu Usman