1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin Somalia

December 31, 2006
https://p.dw.com/p/BuVw

Prime ministan Somalia ya bayyana cewa mutanen da ake zargi da harin da aka kaiwa ofishin jakadancin Amurka hari a gabashin Afrika ,a shekarata 1998,suna boye a garin a halin yanzu a karkashin gamayyar kotunan musulmin somaliya.Prime minista Ali Mohd Gedi ya fadawa manema labaru cewa yan kungiyar Alqaeda guda uku da ake nema ruwa a jalolo a dangane da hare haren na kasashen Kenya da Tanzania,a wancan lokascin suna boye a garin Kismayo,kuma a shirye suke wajen nemosu domin kashe su.Mr Gedi yace a yau ya zasnta da jakadan Amurka na Kenya Michael Ranneberger,adangane inganta matakan tsaro kann iyakokin somaliya da Kenya,domin kada wadanda ake zargin su tsere takan iyaka.