1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mali: Rikicin Fulani da 'yan kabilar Dogon

Abdourahamane Hassane LMJ
June 26, 2018

Tashin hankalin da ake faman yi tsakanin Fulani da 'yan kabilar Dogon na Mali ya shiga wani sabon yanayi bayan da aka kai hari a kan fararen hula guda 30 Fulani.

https://p.dw.com/p/30L7b
Mali na fama da rikice-rikice
Mali na fama da rikice-rikiceHoto: AP

Yanzu haka dai hukumomin Mali na kokarin shawo kan matsalar, sai dai kuma suna fuskantar suka daga 'yan adawa a kan wannan batu. Tun lokacin da aka fara yin tashin hankalin gwamnatin Mali ta sanar da cewar ta jibge sojoji a garin na Koumaga, inda ake faman yin tashin hankalin tsakanin Fulani da 'yan kabilar Dogon. Yanzu haka jam'ian gwamnati biyu na kasar ta Mali sun isa yankin domin kwantar da hankula. Babbar matsalar dai shi ne cewar wasu kabilun Fulanin na zargin hukumomin da nuna goyon baya ga maharban Dozos 'yan kabilar Dogon. 'Yan adawa dai na Malin na zargin gwamnatin da saka siyasa a cikin wannan rikici. Shekaru uku ke nan da suka wuce yankin Tsakiyar na Mali yake fama da tashin hankali na fadan da ake yi tsakanin makiyaya da Fulani da 'yan kabilar Bambara da kuma Dogon wadanda galibinsu manoma ne.