1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin ƙabilanci a arewa maso tsakiyar Najeriya

November 22, 2012

Tashin hankali a tsakanin 'yan ƙabilar Eggon da Kwaro dake garin Agyaragu cikin jihar Nassarawa, ya janyo hasarar dukiya da rayukan mutane akalla takwas.

https://p.dw.com/p/16oDE
A picture taken on April 18, 2011 shows Nigerian police enforcing a curfew in the capital of Bauchi state, nothern Nigeria, after riots, run by muslim youth, broke out in Bauchi. Nigeria's Goodluck Jonathan has been declared winner of presidential elections in a landmark vote that exposed regional tensions and led to deadly rioting in the mainly Muslim north. Jonathan, the incumbent and first president from the southern oil-producing Niger Delta region, won 57 percent of the vote in Africa's most populous nation, easily beating his northern rival, ex-military ruler Muhammadu Buhari. AFP PHOTO / Tony KARUMBA (Photo credit should read TONY KARUMBA/AFP/Getty Images)
Hoto: Getty Images/AFP

Rahotannin baya-bayan nan dai sunce koda da safiyar wannan Alhamis ma dai wani rikicin ya kuma sake ɓarkewa tsakanin 'yan ƙabilar ta Eggon da Kwaro, inda akayi ƙone-ƙonen gidaje tare da hassarar rayuka da dama, kuma ya zuwa yanzu akasarin mutanen da suka sami raunuka an kaisu asibitin kwararu na Dr. Ɗalhatu Arab dake cikin garin lafiya domin samun jiyya.

Hasali ma dai rikicin ya taso ne sakamakon zargin wani matashi da satar Babur daga Unguwar Yakubu dake cikin garin Agyragu inda kuma yaje ya sayar da Babur ɗin a Ungwar kwaro dake garin na Agyaragu, kuma bayan gano babur ɗin ne sai yamutsi ya tashi tsakanin ɓangarorin ƙabilun biyu.

Kasancewar matasa daga ƙabilun ne wannan lamari ya shafa, wani dana zanta dashi ta wayar tarho dake da zama a Unguwar Yakubu cikin garin Agyragu yace dani an soma rikicin ne a gaban sa.

Nayi ƙoƙarin samun alƙaluma don sanin adadin mutane da suka mutu ta hanyar jami'an 'yansanda, to amma hakan yaci tura domin acewar su akwai waɗanda rikicin kan ritsa dasu a wajen gari wanda kuma basu da cikakken rahoto kai, to sai dai wani dattijo a ƙauyen daya nemi in sakaya sunan sa, yace dani yana shirin yaje garin Lafiya ne domin gujewa tashin hankalin kuma ya tabbatar min da mutuwar mutane takwas agarin na Agyaragu.

Soldier patrol to monitor protesters at Ojota district in Lagos on January 16, 2012. Nigerian security forces fired tear gas and shot into the air Monday to disperse around 300 protesters in Lagos as authorities moved to prevent demonstrations in various parts of the country. Nigerian unions announced on January 16 they were suspending a week-old nationwide strike over fuel prices which has shut down Africa's most populous nation and brought tens of thousands out in protest. AFP PHOTO/PIUS UTOMI EKPEI (Photo credit should read PIUS UTOMI EKPEI/AFP/Getty Images)
Hoto: Getty Images/AFP

Rahotanni sunce ƙone-ƙonen da akayi a wannan Larabar, ya ritsa da gidajen wasu manya-manyan jami'an gwamnatin jihar Nassarawa. Na tautaunawa da kakakin gwamnatin jihar kan al'amura na mussaman Abdulhamid Kwarara wanda yace dani da safiyar yau suka je garin na Agyaragu tare da mataimakin gwamnan jihar, kuma yayi min karin bayani ta wayar tarho daga can kauyen na Agyaragu.

Yanzu haka dai an tura wasu ƙarin jami'an tsaro dake sintiri tsakanin Lafiya zuwa garin na Agyaragu mai nisan kilomita 20, daga birnin Lafiya, don tabbatar da ganin rikicin ya lafa.

Mawallafi : Abdullahi Maidawa
Edita : Saleh Umar Saleh