1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Gini: Rikici ya barke bayan baiyana sakamakon babban zabe

Ramatu Garba Baba
October 23, 2020

Rahotanni na nuni da cewa rikici ya barke a tsakanin masu zanga-zangar adawa da sakamakon babban zaben kasar da ke nuni da cewa, Shugaba mai ci Alpha Conde ne ya samu nasara a zaben na makon jiya.

https://p.dw.com/p/3kM8T
Guinea Ausschreitungen nach Bekanntgabe der vorläufigen Ergebnisse in Conakry
Hoto: John Wessels/AFP

'Yan sanda sun yi amfani da hayaki mai saka kwalla a tarwatsa masu zanga-zangar adawa da sakamakon babban zaben da ya bai wa Shugaba mai ci Alpha Conde nasara. Rahotanni na cewa, an yi arangama a tsakanin jami'an tsaro da magoya bayan madugun adawa Cellou Diallo a unguwar Sonfonia da ke Konakry, babban birnin kasar.


Kididdigar da hukumar zaben kasar ta fita ya nunar da cewa,  Shugaba Conde ya lashe zaben da wagegen tazara gabanin babban abokin hamayyarsa Cellou Dalein Diallo a zaben da aka gudanar a karshen makon da ya gabata. Ana dai zargi mahukuntan Ginin da bayar da umarnin datse kafar intanet bayan barkewar rikicin na wannan Juma'ar, wanda kuma ba sabon abu bane da gwamnatin ta saba yi a duk lokacin da aka sami barkewar rikici a kasar..