1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sama da mutane 50 sun halaka

Binta Aliyu Zurmi
January 28, 2020

Akalla mutane hamsin ne suka rasa rayukansu a wani rikicin kabilanci da ya barke tsakanin kungiyoyi biyu masu gwagwarmaya da makamai a garin Bria da ke Jamhuriyar Afirka ta tsakiya, inji wani babban jami'in kasar.

https://p.dw.com/p/3Wvft
Zentralafrikanische Republik - Antibalaka Kämpfer
Hoto: Getty Images/AFP/A. Huguet

Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya dai na ci gaba da fama da rigingimun kabilanci da na addini, a tsakanin masu gwagwarmaya da makamai, duk da kasancewar rundunar samar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya a kasar.

Rahotanni na cewar sama da kashi biyu na yankunan kasar na karkashin ikon masu gwagwarmaya ne, rikicin da ya yi wa kasar katutu, ba ya rasa nasaba da kokarin mallakar albarkatun kasa da Allah ya huwacewa kasar.